Back

Ƴan Najeriya, kada ku kula da rubuce-rubuce a Facebook masu yaudarar ku cewa ‘ ku cike takardar neman tallafin karatu na Dangote’

A TAƘAICE: Rubuce-Rubuce da dama a Facebook na iƙirarin cewa ƴan Najeriya masu sha’awa zasu iya cike neman tallafin rukunin kamfanin Dangote. Ayi watsi da hakan.

“Tallafin karatu na Dangote ga ƴan Najeriya. Ku nema a nan,” saƙon na Facebook ke cewa

Saƙon na haɗe da wajen da za’a latsa wato link da zai kai mutum wani shafin yanar gizo da masu buƙatar tallafin zasu iya cike izinin nema. 

Aliko Dangote shine shugaban rukunin kamfanunnukan Dangote, babban mai samar da siminti, kuma babban mafi girman ɗan kasuwa a Yammacin  Afrika. 

Mujallar Forbes ta bayyana Dangote a matsayin mutum mafi ƙarfi a Afrika. Mujallar Time kuma tace shine mutum mafi tasiri a duniya

Shine kuma daraktan gidauniyar Aliko Dangote, wadda ke tallafawa mutane a fannin lafiya da ilimi. 

Mun ci karo da makamanciyar da’awar a nan da nan. (A lura: Za’a samu wasu misalan a ƙarshen wannan rahoton.)

Shin ƴan Najeriya zasu iya neman “tallafin karatu na Dangote” ta hanyar amfani da link ɗin da aka samar? Mun bincika. 

Dangotescholarship_scam

Babu dangantaka da Dangote

Africa Check ta latsa link ɗin har ya kaimu ga wani shafin yanar gizo mai taken: “Ku fara neman izini.” Yana kuma da wani koren abun latsawa da ke cewa “KU NEMA A NAN” aka kuma bayyana ranar “16 ga watan Yuli, 2024” a matsayin ranar da wa’adin neman tallafin zai cika.

Mun latsa koren wajen latsawar ya kuma kai mu wani shafin yanar gizo na blog mai ɗauke da izinin neman aiki a ƙasar Australia daban-daban da kuma yadda za’a nema. 

Mun duba shafin yanar gizo na Dangote da kuma shafukan kafafen sada zumunta na gidauniyar, amma bamuga wani abu makamancin sanarwar neman tallafin ba. Link ɗin na daga cikin abun da wasu mutane keyi don neman masu shiga shafi, don cimma manufar su ta neman a sansu da kuma samun yawan masu shiga shafi. 

Don kiyaye kan ku, ku karanta hanyoyin da muka jero muku don kare kai daga zamba a Facebook da yadda zaku iya gano ta. 

An samu makamanciyar wannan da’awa a nan, nan, nan, nan, nan, nan, nan da nan


 

For publishers: what to do if your post is rated false

A fact-checker has rated your Facebook or Instagram post as “false”, “altered”, “partly false” or “missing context”. This could have serious consequences. What do you do?

Click on our guide for the steps you should follow.

Publishers guide

Africa Check teams up with Facebook

Africa Check is a partner in Meta's third-party fact-checking programme to help stop the spread of false information on social media.

The content we rate as “false” will be downgraded on Facebook and Instagram. This means fewer people will see it.

You can also help identify false information on Facebook. This guide explains how.

Add new comment

Restricted HTML

  • Allowed HTML tags: <a href hreflang> <em> <strong> <cite> <blockquote cite> <code> <ul type> <ol start type> <li> <dl> <dt> <dd> <h2 id> <h3 id> <h4 id> <h5 id> <h6 id>
  • Lines and paragraphs break automatically.
  • Web page addresses and email addresses turn into links automatically.
limit: 600 characters

Want to keep reading our fact-checks?

We will never charge you for verified, reliable information. Help us keep it that way by supporting our work.

Become a newsletter subscriber

Support independent fact-checking in Africa.